1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar OSCE ta hango wata barazana a rikicin Ukraine

Muntaqa AhiwaFebruary 27, 2015

Ƙungiyar OSCE ta ƙasashen Turai ta yi gargaɗin kan yiyuwar ɓarkewar sabon faɗa a Ukraine

https://p.dw.com/p/1Ej08
Ukraine Kiew Maidan Spendensammlung Armee Propaganda
Hoto: DW/Erik Albrecht

Manzon musamman na ƙungiyar nan ta tsaro da haɗin kan ƙasashen Turai wato OSCE da ke ƙasar Ukraine, ta yi gargaɗi kan yiwuwar ɓarkewar sabon faɗa a Ukraine, a dai dai lokacin da ake batu na tsagaita buɗa wuta a gabashin Ukraine ɗin.

Jami'ar diflomasiyar wato Heidi Tagliyavina, da ta shaidawa kwamitin tsaron Majalisar Ɗinkin Duniya cewa akwai alamun dakatar da faɗa a gabashin Ukraine ɗin tare ma da sakin fursunoni da janye manyan makamai, ta ce ta hango alamun taɓarɓarewa lamura a yankin, don a cewarta ko a yau Jumma'a ma sai da aka kashe sojojin Ukraine uku a wata fitina da ta kaure tsakaninsu da 'yan tawaye magoya bayan Rasha.