1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a gudanar da bincike kan rikicin Gaza

July 23, 2014

Hukumar kare hakkin bani adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta amince da fara gudanar da bincike kan irin luguden wutar da Izra'ila ke yi a Gaza sakamakon rikicinta da Hamas.

https://p.dw.com/p/1Chha
Gaza Ruine 22.7.2014
Hoto: Said Khatib/AFP/Getty Images

Wannan dai ya biyo bayan korafin da Falasdinu ta gabatar gaban hukumar mai mambobi 46, inda 29 daga cikin mambobin da suka hada da kasashen Larabawa da Rasha da China da kasashen Latin Amirka da na nahiyar Afirka sun amince da gudanar da binciken.

To sai dai Amirka ta kada kuri'ar kin amince da kudurin yayin da kasahen Turai galibinsu na kungiyar EU suka yi rowar kuri'unsu. Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da kasashen duniya ke cigaba da neman ganin an kawo karshen zub da jinin da ake yi.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Zainab Mohammed Abubakar