1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga a Hong Kong

Abdourahamane HassaneNovember 26, 2014

Wata kotu a Hong Kong ta ba da umarni ga jami'an tsaron da su kori jama'ar da suka mamaye wani dandalin.

https://p.dw.com/p/1DtmN
Hongkong Räumung nach Protest 25.11.2014
Hoto: Reuters/Bobby Yip

An yi taho mu gama tsakanin 'yan sanda da masu yin bore a Hong Kong a lokacin da masu ɗamara suka durfafi jama'ar da suka datse wani dandalin, wanda wata kotun ta ba da umarnin korar jama'ar da ke yin zaman dirshan a kansa.

'Yan sandan sun kama mutane kusan guda 80 a ciki har da wasu shugabaniin ɗaliban guda biyu masu fafutukar neman sauyi na demokaraɗiyya a Hong Kong ɗin.