1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sanda sun buɗe wuta a kan masu bore a Burkina

Abdourahamane HassaneOctober 30, 2014

Rahotannin da ke zuwa mana daga Burkina Faso na cewar jami'an tsaro sun buɗe wuta a kan daubban jama'a masu zanga- zanga a lokacin da suke ƙoƙarin danawa fadar shugaban ƙasar.

https://p.dw.com/p/1DeXQ
Burkina Faso Protest Ausschreitungen Parlament Brand
Hoto: Getty Images/ AFP/ Issouf Sanogo

Tun farko masu yin boren sun ƙone ginin majalisar dokokin ƙasar a yau,a dai dai lokacin da aka shirya majalisar za ta tattauna ƙudirin bai wa shugab Blaise Compaore damar yin takara a a zaɓen shugaban ƙasar wa'adi na biyar.

Sannan kuma a garin Bobo Dioulasso, birnin na biyu mafi girma na ƙasar an ba da rahoton cewar an ƙone ofishin magajin garin birnin da kuma cibiyar jam'iyyar da ke yin mulki.