1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Amirka sun kai sabon hari kan IS a Iraki

Mohammad Nasiru AwalMarch 26, 2015

Sojojin saman Amirka da ke jagorantar kawancen yaki da mayakan IS da ke ikirarin Jihadi, sun kai farmaki kan sansanoninsu da ke Tikrit.

https://p.dw.com/p/1Ey0M
Irak Tikrit Offensive gegen IS
Hoto: Reuters/T. Al-Sudani

Sojojin kawancen yaki da mayakan kungiyar IS masu da'awar kafa daular Islama, sun sake kai farmaki kan sansanonin masu ikirarin jihadin a Iraki. Kakakin ma'aikatar tsaro a birnin Bagadaza ya ce jiragen saman yakin karkashin jagorancin Amirka sun kuma samu tallafi daga sojojin Iraki. A ranar Laraba ma Amirka ta kai hare-hare a birnin Tikrit da ke zama mahaifar tsohon shugaban Iraki Saddam Hussein. Tun a cikin watan Yunin bara mayakan IS suka mamaye birnin na Tikrit, kuma tun kimanin makonni hudu ke nan sojojin Iraki ke kokarin karbe iko da birnin.