1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojan Kamaru sun kashe mayakan Boko Haram 40

September 2, 2014

An tafka wata musayar wuta tsakanin sojojin Jamhuriyar Kamaru da mambobin kungiyar Boko Haram ta Najeriya

https://p.dw.com/p/1D5Rq
Kamerun Soldaten gegen Boko Haram
Hoto: Reinnier KAZE/AFP/Getty Images

Jamian tsaro a Jamhuriyar Kamaru sun bayyana cewa sun kashe a kalla mayakan kungiyar Boko Haram 40, wadanda suka kutsa kasar daga Najeriya ta yankin arewa mai nisa.

Bayan wani harin roka kan sojojin na Kamaru da ke yankin Fotokol da mayakan na Boko Haram suka kai, mai magana yawun sojan na Kamaru ya bayyana cewa mayakan sakan na kungiyar Boko Haram sun ja da baya zuwa Najeriya bayan wani gumurzun da suka tafka.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Umaru Aliyu