1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya ta kori jami'an Majalisar Ɗinkin Duniya a ƙasarta

Muntaqa AhiwaFebruary 27, 2015

Gwamnatin Siriya ta kori jami'an Majalisar Ɗinikin Diniya da ke kasarta

https://p.dw.com/p/1Eizx
Staffan de Mistura / Syrien / UN
Hoto: picture-alliance/AA

Gwamnatin ƙasar Syria ta kori wasu jami'an Majalisar Ɗinkin Duniya uku daga ƙasarta a dai lokacin da mai shiga tsakani na majalisar t ke daf da ziyartar ƙasar don tattauna yiwuwar Syriyar ta tsagaita kai hare-hare kan birnin Aleppo. Wannan matakin ana ganin zai kawo tarnaƙi ga samar da tallafi a ƙasar, a lokacin kuma da ake kan buƙatar haka.

Ana dai saran ziyarar ta Staffan de Mistura mai shiga tsakanin na MDD a gobe Asabar za ta yi tasiri ga buƙatar tsagaita kai hare-hare kan Aleppo da ke arewacin ƙasar na makonni shida.