1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin kammala yakin zabe a Tunisiya

December 19, 2014

A wannan Jumma'a ce ake kawo karshe yakin neman zabe a Tunisiya, a shirye-shiryen da ake yi na gudanar da zaben shugaban kasa zagaye na biyu a ranar Lahadi mai zuwa.

https://p.dw.com/p/1E7UD
Hoto: DW/Tarek Guizani

Akalla 'yan kasar Tunisiya kusan Milian biyar ne da dubu dari uku, suka cancanci su yi zabe. Tuni ma 'yan kasar ta dake kasashen ketare suka fara kada kuri'unsu tun daga wannan Jumma'a.

Za su zabi tsakanin 'yan takara biyu da suka hada da shugaban kasar mai barin gado Moncef Marzouki, da kuma Béji Caïd Essebsi, da yazo na daya a zaben shugaban kasar zagaye na farko. 'Yan takarar biyu dai sun shirya gudanar da wasu manya-manyan tarurrukan gangami a yammacin wannan Jumma'a a Tunis babban birnin kasar ta Tunisiya.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Umaru Aliyu