1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shekaru 20 da kisan kare dangi a Ruwanda

April 10, 2014

Kasashen duniya sun hade da al'ummomin kasar Ruwanda, wajen nuna alhini kan mutane sama da dubu 800 da aka yi wa kisan kiyashi a shekara ta 1994.

https://p.dw.com/p/1Bflh
Ruanda Genozid Gedenkfeier 07.04.2014 Trauer
Hoto: Getty Images

Shekaru 20 bayan kisan kiyashin da aka yi wa 'yan kabilar Tutsi a kasar Ruwanda a shekara ta 1994, har kawo yanzu wadanda suka shaida wannan balahira na ci gaba da tuna dinbin tashin hankalin da suka gani a wannan lokaci. Mutane kamar su François Kabagema da a yanzu haka yake da kimanin shekaru 45 a duniya ya bayyana yadda ya shaidawa idanunsa yadda aka rika kashe mutane a yayin da yake ofishin jakadancin kasar Faransa a birinin Kigali na kasar Ruwandan. Zaku iya samun karin bayani a jerin rahotanni da ke cikin wannan kundi, kan wannan hali da al'ummar kasar ta tsinci kanta, da ma irin yadda dangantaka ta yi tsami da kasashen da Ruwandan ta yi zargi da hannu a kisan kare dangin.