1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nasarar yaki da Ebola

January 29, 2015

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta sanar da cewa kwararru a fannin lafiya sun mayar da hankali wajen kawo karshen yaduwar annobar cutar Ebola mai saurin kisa maimakon rage yaduwarta.

https://p.dw.com/p/1ESt0
Hoto: , Francisco Leong/AFP/Getty Images

Hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa a karon farko tun cikin watan Yuni, a makon da ya gabata an samu raguwar wadanda ke kamuwa da cutar a kasashe uku da cutar tafi kamari a cikinsu wato Guinea da Saliyo da kuma Laberiya. Hukumar ta kara da cewa kaso 30 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar a Guinea da kuma kaso 50 cikin 100 a Laberiya ne kadai aka hakikance sun yi mu'amala da masu cutar ta Ebola, wanda hakan ya sanya tunanin a kan yadda mutane ke kamuwa da ita. Cutar dai kawo yanzu ta hallaka sama da mutane 8,000 tun bayan da ta bulla a yankin yammacin Afirka cikin farkon shekara ta 2014 da ta gabata.

MAwallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu