1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon ofishin yaƙi da Ebola a Afirka

Usman ShehuSeptember 20, 2014

Za a girka ofishin ne domin ƙara azama bisa yaƙi da cutar ta Ebola, yanzu za'a kawo jami'an kula da lafiya kusa da ƙasashen da ke fama da cutar.

https://p.dw.com/p/1DGCy
Ebola in Liberia
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Jallanzo

A cewar Majalisar Ɗinkin Duniya za ta buɗe ofishin yaƙi da cutar Ebola a yammacin Afirka wanda zai kasance a Accra babban binrin ƙasar Ghana, amma za su buɗe rassa a ƙasashen Laberiya, Saliyo da Gini. Sakatare janar na MDD Ban Ki-Moon, ya ce rashin fahimtar yanayin da ake kamuwa da cutar ya hana ɗaukar matakin daƙile annobar da yanzu ta hallaka mutane sama da 2600. Dubban jami'an kiwon lafiya a ƙasar Saliyo na ci gaba da binciken gida-gida domin zaƙulo waɗanda suka kamu da cutar ta Ebola.