1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon fada ya barke a Sudan ta Kudu

October 29, 2014

Ana ci gaba da fafatawa tsakanin bangarorin da ke rikici a kasar Sudan ta Kudu.

https://p.dw.com/p/1De8t
Hoto: Reuters

An yi kazamin dauki ba dadi tsakanin sojojin kasar Sudan ta Kudu da mayakan 'yan tawaye a garin Bentiu mai arzikin man fetur, domin kwace garin daga hannun dakarun gwamnatin. Sojoji da ma'aikatan agaji sun tabbatar da faruwar lamarin. Wani kakakin soji ya ce an kai hare-hare daga kudanci da arewacin birnin.

Sabon fadan ya kawo karshen tsagaita wutar da aka samu tsakanin bangarorin biyu na Shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar. Duk bangarorin na kasar Sudan ta Kudu suna karkashin matsin lamba na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, tun bayan barkewar rikici a watan Disamba.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe