1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabbin hare-hare a garuruwan Izge da Malari da ke a jihar Borno

February 23, 2014

Hare-haren waɗanda da ake zaton cewar 'yan Ƙungiyar Boko Haram ne suka kai su, a garuruwan da ke a yankin arewa maso gabashin Najeriya an kashe mutane da dama.

https://p.dw.com/p/1BED0
Nigeria Boko Harem Angriff in Damaturu
Hoto: picture-alliance/AP

Wasu maharan da ake zaton 'yan Ƙungiyar Boko Haram ne sun kai wasu sabbin hare-hare a garuruwan Izge da Malari a jihar Borno da ke a yanki Arewa maso gabashin Tarrayar Najeriya. Mazauna garin Izge da yanzu haka suka tsere sun bayyana cewar 'yan bindigar sun yi ta yin luguden wuta a garin har sai da suka tabbatar duk wani mai motsi ya ƙare tare da ƙona garin ƙurmus.

Yanzu haka dai babu kowa a garin na Izge wanda ya sha fama da hari a makon da ya gabata wanda a cikin aka samu hasarar rayuka sama da 100. 'Yan bindigar sun kai hari kuma a garin Malari mai nisan kilomita 15 daga Maiduguri, babban birnin jihar inda ake da fargabar an samu hasarar rayuka da dama.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman