Wani harin ta'addanci da aka kai a ofishin jami'an tsaro a Jamhuriyar Nijar ya yi sanadiyyar rasuwar jami'in jandarma guda tare da jikkata wasu guda biyu. Harin dai wasu mutane ne da ba a san ko su wanene ba dauke da bindigogi suka kai shi a ofshin jami'an tsaron na jandarma da ke garin Banibangou.