1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 24 suka rasu a zanga-zangar Burkina Faso

November 26, 2014

Kwamitin da ya tattara bayanai kan irin asarar da ta biyo bayan zanga-zangar Burkina Faso da ta yi awon gaba da gwamnatin Blaise Compaore ya mika rahotonsa.

https://p.dw.com/p/1Du6g
Burkina Faso Protest Ausschreitungen Parlament Brand
Hoto: Getty Images/ AFP/ Issouf Sanogo

Masu zanga-zangar da suka fusata da tsawon wa'adin mulkin Blaise Compaore da ya nemi a kara masa wa'adin mulki bayan kusan shekaru 30 yana dare bisa kan mulki sun sanya wuta a majalisar dokokin kasar da ma tilastawa tsohon shugaban sauka daga kujerar sa a ranar 31 ga watan Oktoba da ta gabata.

Clarisse Ouoba, da ta jagoranci kwamitin ta bayyana wa manema labarai cewa mutane 24 ne suka rasu a lokacin zanga-zangar a yayin da wasu sama da dari shida suka samu raunika sannan an afkawa gidajen wasu ministoci da 'yan majalisa inda aka yi musu sace-sace. ko da ya ke tun da fari 'yan adawa sun ce mutane talatin ne suka rasu a rikicin.

Yanzu dai gwamnatin rikon kwarya ke jan ragamar mulkin wannan kasa da ke a yammacin Afrika a inda ake saran gudanar da zabe a shekara me zuwa.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Umaru Aliyu