1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kyama ga likitocin Ebola

Lateefa Mustapha Ja'afarDecember 20, 2014

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci da a guji kyamatar likitocin da ke kula da masu cutar Ebola, musamman a kasashen da cutar ta fi kamari.

https://p.dw.com/p/1E87E
Ban Ki-moon in Liberia 19.12.2014
Hoto: Reuters/J. Giahyue

Majalisar ta yi kiran ne ga kasashen da ke fama da annobar cutar Ebola mai saurin kisa a yankin yammacin Afirka, inda ta ce likitocin na yin aiki tukuru domin ganin an kawo karshen cutar. Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniyar Ban Ki-moon ne ya yi wannan kira a yayin da ya isa kasar Guinea a rana ta biyu ta ziyarar da yake yi domin bayyana godiyarsa ga likitocin da ke kula da masu Ebolan a kasashen da cutar ta fi kamari. Kididdigar baya-bayan nan da Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fitar dai, ta nunar da cewa kawo yanzu mutane dubu 7,373 ne suka rasa rayukansu sakamakon Ebola a kasashe uku da cutar ta fi kamari a yankin yammacin Afirka. Ban Ki-moon dai ya fara ya da zango ne a Laberiya kafin daga bisani ya isa kasar Saliyo, inda a Asabar din nan ya isa kasar Guinea yayin da kuma zai kammala ziyarar ta sa a sansanin jami'an yaki da cutar Ebola na Majalisar Dinkin Duniya (UNMEER) da ke kasar Ghana bayan ya ziyarci kasar Mali.