Kotu a Jamus ta daure wani dan fashin teku
April 17, 2014Talla
Mutumin wanda kotun ba ta bayyana sunansa ba na daga cikin wanda suka jagoranci fashin jirgin da yin garkuwa da wadanda ke cikinsa har ma suka azabtar da su na tsawo wattani takwas, kafin daga bisani su sako su bayan da kamfanin jirgin ruwan ya biya kudin fansa har euro miliyan uku da rabi.
A cikin shekarar da ta gabata ce dai aka kama mutumin dan shekaru 44 da haihuwa yayin da ake tanance zanen yatsunsa na hannu daidai lokacin da ya yi amfani da takardun bogi wajen neman mafaka irin ta 'yan gudun hijira a nan Jamus.
Kotun dai ta bashi mako guda na ya daukaka kara idan har bai amince da hukuncin ba.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammed Awal Balarabe