1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamen jami'an FIFA a Switzerland

Yusuf BalaMay 27, 2015

Ofishin shari'a na kasar Switzerland ya nunar da cewa jami'an Amirka na zargin jami'an hukumar kwallon kafa ta duniya da karbar cin hanci da rashawa gabannin taron da FIFA za ta yi a Zurich nan gaba.

https://p.dw.com/p/1FWx3
Schweiz FIFA Schriftzug Hauptquartier in Zürich
Hoto: Getty Images/AFP/M. Buholzer

An tsare wasu jami'an hukunmar kwallon kafa ta duniya FIFA a Switzerland in da za a tisa keyarsu zuwa Amirka saboda zargin wata almundahna ta cin hanci da rashawa.

Ofishin shari'a na kasa a Swiss ya bayyana cewa an tsare jami'ai shida daga hukumar ta FIFA inda za a ci gaba da dakon ji daga bangaren Amirka ko za ta bukaci a mikasu gareta kafin babban taro da hukumar ta FIFA ta tsara yi a Zurich.

A bayanan da ofishin shari'a na kasar ta Switzerland ya fitar a ranar Laraban nan, ya nunar da cewa jami'an Amirka na zarginsu da karbar cin hanci na makudan miliyoyin daloli.

Ya ce ofishin mai shari'a a gabashin New York na gudanar da bincike kan wadannan jami'ai inda ake samun hannunsu a badakalar cin hanci da rashawa tun daga shekarun 1990 zuwa yanzu.

Ita ma dai Amirkar a yanzu ta bayyana cewa za ta gudanar da bincike kan wadannan jami'ai.