1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jiran tsammani wa Rabbuka a Chibok

Mohammad Nasiru AwalApril 16, 2015

A cikin daren ranar 14 ga watan Afrilun shekarar 2014 Boko Haram ta sace 'yan mata fiye da 200 daga wata makarantar sakandare na garin Chibok.

https://p.dw.com/p/1F9Pt
Nigeria Schicksal der entführten Chibok Mädchen
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Palitza

A cikin daren ranar 14 ga watan Afrilun shekara ta 2014 mayakan kungiyar Boko Haram suka sace 'yan mata fiye da 200 daga wata makarantar sakandare na garin Chibok da ke jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya, kuma har yanzu iyaye da 'yan'uwansu na zaman jiran tsammani wa Rabbuka.