1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ISIS ta ƙwace iko da Al-Muthanna

July 9, 2014

An ba da rahoton cewar mayaƙan Ƙungiyar ISIS masu kaifin kishin addini sun ƙwace iko da wani tsohon runbu ajiye makamai masu guba tun na lokacin Saddam Hussein da ke a garin Al-Muthanna

https://p.dw.com/p/1CYX9
Irak - Junge Männer werden zur Verteidgung rekrutiert
Hoto: Getty Images

A cikin wata wasiƙa da gwamnatin Iraƙi ta aike da ita ga babban sakataran Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki-Moon tun a farkon wannan wata,ta tabbatar da cewar 'yan tawayen sun karɓe iko da cibiyar ta Al Muthanna da ke a yanki arewa maso yammancin birnin bagadaza.

Jakadin Iraƙi a Majalisar Ɗinkin Duniya Mohammed Ali Alhakim ya ce sakamakon rashin tsaro Iraƙin ba za ta ci gaba ba, da shirinta na lalata makaman masu guba har sai al'amura sun sake daidaita.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu