1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta yi kira da a dakatar da matakan soji a Yemen

Mohammad Nasiru AwalMarch 26, 2015

Saudiyya ce ke jagorantar taron dangin da kasashen Larabawa suka yi wa mayakan Huthi da suka lashi takobin kifar da shugaba Mansour Hadi.

https://p.dw.com/p/1EyCK
Saudi-Arabien Kämpfe mit Huthi Rebellen an der Grenze zu Jemen
Hoto: imago/Xinhua

Kasar Iran ta yi kira da a dakatar da matakan sojin da kasar Saudiyya ke jagoranta kan kasar Yemen. An jiyo ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif na cewa kasarsa za ta yi duk abin da ya dace na shawo kan rikicin na kasar ta Yemen. A kuma wata hira da ya yi da Firaministan Birtaniya David Cameron ta wayar tarho, shugaban Iran Hassan Rouhani ya soki matakin sojin da ake dauka kan Yemen din. Jiragen saman yakin Saudiyya da kawayenta na kasashen Larabawa sun kai hare-hare kan dakarun Huthi da ke kokarin kifar da shugaban Yemen Abd-Rabbu Mansour Hadi mai samun daurin gindin kasashen yamma. A kuma halin da ake ciki shugaba Mansour Hadi ya sauka birnin Riyadh na Saudiyya.