1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hong Kong: An yi barazanar fadada bore

Ahmed SalisuSeptember 30, 2014

Masu rajin neman ganin an girka dimokradiyya a Hong Kong sun ce za su fadada boren su muddin jagoran yankin bai zauna da su kan teburin shawarwari a wannan Talatar ba.

https://p.dw.com/p/1DNkZ
China Studentenprotest in Hongkong Occupy Central Regenschirme und Polizei
Hoto: Reuters/B. Yip

Sakataren kungiyar daliban Hong Kong din Alex Chow ya ce muddin jagoran Hong Kong din Leung Chun-ying ya gaza fita zuwa dandalin nan na Civic Square kafin tsakar daren yau, to kuwa karin dubban mutane na yankin za su bazama kan tituna don neman ganin an biya musu bukata.

Mr. Chow ya ce dalibai a halin yanzu na duba yiwuwar kara daukar mataki kan wannan fafutuka da ake yi inda ya kara da cewar in hakarsu ba ta kai ga cimma ruwa ba to za su tabbatar an yi yajin aikin gama-gari a Hog Kong din da kuma mamaye gine-gine gwamnati baki daya.