1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin Isra'ila ya ta'azzara a Zirin Gaza

July 29, 2014

Da sanyin safiyar wannan Talatar ce jiragen yaki na sama da na ruwa da tankunan yakin Isra'ila, suka yi kalaci da abun da suka kira yankunan 'yan Hamas.

https://p.dw.com/p/1Ckyc
Gaza Hafen Bombardierung Israel Explosion 29.7.
Hoto: Reuters

Dakarun Isra'ilan dai sun dauki tsawon daren jiya suna kai harin bama-bamai a Zirin Gaza, wanda ke zama mafi munin harin da suka kai a wannan yanki makonni uku da kaddamar da wannan fada. Sababbin somamen Isra'ilan na zuwa ne, bayan da Fraiminista Benjamin Netanyahu ya yi gargadin yiwuwar tsawaita hare haren nasu a Gaza.Tuni dai babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira da a gaggauta tsagaita wuta:

"Lokaci ya yi na tsagaita wuta ba tare da bata lokaci ba, domin kare rayukan al'umma. Sabo da halin da mutane suke ciki ya zamanto wajibi a tsayar da wannan fada. Wannan fada ya yi sanadiyyar rayukan Falasdinawa sama da 1,000, akasarinsu fararen hula, daruruwansu kuwa yara kanana. A daya hannun kuma harin rokokin Hamas ya yi sanadiyyar rayukan fararen hula uku na Bani Yahudu".

Tun a daren jiyan ne dai, sararin samaniyan Gaza ya turnuke da hayaki, sakamakon hare-haren dakarun na Isra'ila babu kakkautawa.

Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Usman Shehu Usman