1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hama Amadou ya tsere daga Nijar

Usman ShehuAugust 28, 2014

Shugaban majalisar dokokin jamhuriyar Nijar kana shugaban jamyyar adawa ta Lumana Afirka Malam Hama Amadou ya tsere zuwa kasar Burkina Faso.

https://p.dw.com/p/1D2vt
Hama Amadou
Hoto: DW/S. Boukari

A cewar wakilinmu Gazali Abdou Tasawa, kafofin yada labarai na radiyo da talabijin mallakar gwamnatin kasar ne suka tabbatar da wannan labari a daran jiya Laraba, ba tare da wani karin bayani ba. Dama dai tun a jiya kwamitin gudanarwa na majalisar dokokin kasar, ya baiwa gwamnatin kasar izinin mika shugaban majalisar dokokin a kotu, domin ya bayar da bahasi akan zargin da ake yi masa na kasancewa da hannu a badakalar cinikin jarirai.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu