1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hama Amadou ya ce gwamnatin Nijar ta yi masa ƙazafi

July 22, 2014

Shugaban majalisar dokokin Nijar kuma shugaban jam'iyyar adawa ta Modem Lumana Afrika ya mayar da martani a karon farko a kan batun badaƙalar cinikin jarirrai da aka zargi maidakinsa.

https://p.dw.com/p/1Cgjy
Hama Amadou shugaban majalisar dokokin Nijar tare da shugaban Nijar Mahamadou IssoufouHoto: BOUREIMA HAMA/AFP/Getty Images

Tun lokacin da jam'iyyar ta Hama Amadou ta Modem Luman Afrika ta fice daga ƙawance jamm'iyyun siyasar masu mulki aka fara kai ruwa rana tsakanin ɓangarorin biyu.

Hulɗa tsakanin sassan biyu ta ƙara dagulewa a baya-baya nan

Dangantaka tsakanin jam'iyyar ta Lumana Afrika da jam'iyyar da ke yin mulki ta ƙara dagulewa, biyo bayan wasu hare-haren da aka kai a gidan matamakin shugaban majalisar na huɗu, da kuma cibiyar jam'iyyar PNDS,Tarayya abin da ya janyo aka tsare wasu magoya bayan jam'iyyar Lumana.

Rahoto a kan martanin Hama Amadou
Hama Amadou, shugaban majalisar dokokin Nijar a tsakiyya.Hoto: DW/M. Kanta

Kafin daga bisanin a bangaɗo wannan lamari na cinikin jarirrai wanda a cikinsa aka cafke mutane 21 waɗanda suka haɗa da maiɗakin shugaban majalisar dokokin.

Hama Amadou ya ƙaryata cewar matarsa na da hannu a cikin lamarin

A lokacin wani taron manema labarai da ya yi shugaban majalisar ya bayyana cewar shugabannin na neman shafa masa kashin kaji ne.

'' Wannan batu na fataucin jarirrai har kawo yanzu babu wasu hujjojin da su ka tabbatar da shi kuma da gaskiyya ne sai su bayyana hujjojin.''

Daga ƙasa za a iya sauraron wannan rahoto

Mawallafi : Gazali Abdou Tassawa
Edita : Abdourahamane Hassane