1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gurɓacewar muhalli a kudancin Najeriya

Abdourahamane HassaneMarch 19, 2015

Ƙungiyar kare hakin bil Adama ta Amnesty International ta bayyana fargabanta dangane da ƙaruwar barazanar da muhali ke fuskanta a Najeriyar.

https://p.dw.com/p/1Et2X
Öl in Nigeria
Hoto: picture-alliance/dpa

Ƙungiyar ta Amnesty ta yi kashedi dangane da bazarnar ƙara samun gurɓacewar muhali a kudancin Najeriyar a sanadiyyar malallar ɗanyan man fetur.Hakan kuwa ya biyo bayan wani rahoton da ƙungiyar ta bayyana wanda a cikinsa ta ce a shekara bara da ta shige ta 2014.

Kamfanon aiki haƙon man fetur ɗin na Shell na Ingila da Eni na Italiya waɗanda ke gudanar da aiyyukansu a Najeriyar sun ce sun haddasa gurɓacewar muhali a wurare 553.Ƙungiyar ta ce wannan addadi da kamfanonin suka bayyana na ɗaga hankali sossai, kuma ta ce ya zama wajibi a farka daga barci tun da sauran wuri.