1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafutukar yaƙi da hamada a Nijar

Mahaman KantaOctober 22, 2014

Ƙungiyar EU na ba da horo ga jami'an ƙungiyoyin farar hulla da na kafofin yaɗa labarai, domi ɗaukar matakkan yaƙi da barazanar mamayewar hamada.

https://p.dw.com/p/1DZuf
Wüste, Sahara, Dürre, Baum, Tod
Hoto: picture-alliance/dpa

Ƙungyiyar tarayyar Turai tare da haɗin gwiwar wasu manyan ƙungiyoyin ne ke ƙaddamar da wannan babban aiki na yin rigakafi ga gurgusowar hamada a Nijar.

A ƙasa da shekaru goma da suka gabata ƙasar ta Nijar ta yi fama da mumunar yanayi na samun koma baya a sha'anin noma da kiwo, duk kuwa hakan na da nasaba ne da gurgusowar hamadar. Wannan shi ya sa ƙasahen duniya suka tashi tsaye haiƙan wajen faɗakar da wakilai na ƙungiyoyi daban-daban domin su kawo tasu gundunmawa domin yin riga kafi.