1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta yi waiwaye kan rikicin Rasha da Ukraine

Usman ShehuJanuary 29, 2015

Ministoshin harkokin wajen Tarayyar Turai za su duba jerin takunkumin karya tattalin arziki da suka aza wa Rasha bisa zargin ta da hannu a rikicin gabashin kasar Ukraine

https://p.dw.com/p/1ESSk
Alexander Sachartschenko Separatistenführer 22.01.2015 Donezk
Hoto: picture-alliance/dpa/TASS/M. Sokolov

A yau Alhamis ne ministocin harkokin wajen za su yi taron nasu. Yanzu haka dai fada tsakanin yan aware da Rasha ke marawa baya da gwamnatin Kiev wanda ke dasawa da kasashen Yamma, yakaru matuka fiye da gabanin sa hannu bisa yarjejeniyar tsakaita wuta da aka yi. Tuni dai jerin takunkumin dama wasu matakan karya tattalin arziki da kasashen Yamma suka dauka kan Rasha, suka fara yin tasiri. Inda a jiya Laraba ministan harkokin wajen Rasha Anton Siluanov, ya ce asarar da su ka yi kawo yanzu ta kai dala biliyan dari biyu.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu