1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola: Dokar hana fita a Saliyo ta fara aiki

September 19, 2014

A wannan Juma'ar ce dokar hana fita ta kwanaki ukun da gwamatin Saliyo ta sanya da nufin yakar cutar nan ta Ebola za ta fara aiki a dukannin yankunan da ke kasar.

https://p.dw.com/p/1DFTu
Ebola in Liberia (Behandlung im Krankenhaus)
Hoto: Issouf Sanogo/AFP/Getty Images

A tsawon wannan kwanakin ministan watsa labaran kasar Alpha Kanu ya ce jami'an kiwon lafiya za su bi gida-gida don fadakar da al'umma kan matakan kare kai daga kamuwa da cutar da ma zakulo wanda cutar ta kama don yi musu magani.

Ma'aikatar kiwon lafiyar kasar ta ce kimanin ma'aikata 30 talatin ne za su kewaya kasar don gudanar da wannan aiki, inda hukumomi ke cewar in har al'umma suka amsa wannan kira to matakin zai taimaka matuka wajen rage bazuwar cutar wadda ta yi sanadin rasuwar mutane da dama a kasar.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Suleiman Babayo