1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kashe mutane a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango

Lateefa Mustapha Ja'AfarApril 24, 2015

Rahotanni daga Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango na nuni da cewa an kashe wasu mutane biyar har lahira cikin dare a yankin Beni da ke gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1FEWs
Kongo, Soldaten der FARDC
Hoto: AFP/Getty Images/A. Wandimoyi

Yankin na Beni dai na zaman wani sashe da 'yan tawayen kasar Uganada ke da karfi. Shugaban yankin na Beni Amisi Kalonda ya shaidawa manema labarai cewa an dad-datsa mutanen ne da adda, sai dai ya ce bashi da wani karin bayani kan kisan nasu. Kisan mutane da adda a garin na Beni dai na neman zama ruwan dare a watannin baya-bayan nan yayin da ake dora alhakin yinsa a kan 'yan tawayen kasar Yuganda da ke nuna adawa da gwamnatin Shugaba Yoweri Museveni na Yuganda.