1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

CDS Rahama na fuskantar barazanar rusawa

July 25, 2014

Ministan cikin gida na Nijar ya gargaɗi jam'iyyar da ta gaggauta yin babban taronta domin sabinta kwamitin gudanarwa na jam'iyyar ko kuma su rusa jam'iyyar.

https://p.dw.com/p/1Cj2H
Mahamane Ousmane 1995 Präsident Niger
Mahamane Ousmane shugaban jam'iyyar CDS RahamaHoto: picture-alliance/dpa

A cikin wata wasiƙa wacce ministan cikin gidan na ƙasar ta Nijar
malam Hasumi Masa'udu wanda shi ne ke kula da harakokin
jam'iyyun siyasa a ƙasar ya aike da ita ga shugaban jam'iyyar ya yi masa kashedi.

Gwamnati Nijar ta ce dole jam'iyyar CDS ta yi babban taronta na ƙasa

Ministan ya gargaɗi shugaban jam'iyyar Mahamane Ousmane da ya kira taron jam'iyyar da gaggawa domin sabinta manbobin kwamitin gudanarwa na jam'iyyar, ko kuma doka ta yi aikinta na soke jam'iyyar kwata-kwata. Wasiƙar gwamnatin dai ta ce ga ƙaida a cikin watanni shida ya zama wajibi jam'iyyar ta gudanar da taronta. Da yake mayar da martani wani jigo daga jam'iyyar ta CDS Alhaji Dudu Rahama cewa ya yi lokacin shirya taron nasu bai yi ba.

Yan tawaye na jam'iyyar sun ce za su kira taron ƙasa na jam'iyyar

Alhaji Abdu Labo mataimakin shugaban jam'iyyar na ƙasa ya bayyana cewar cikin lokaci kaɗan za su gudanar da taron.

Mahamane Ousman Ex-Präsident Niger
Mahamane Ousman a lokacin wani taron manema labaraiHoto: DW/M. Kanta

Daga ƙasa za a iya sauraron wannan rahoto

Mawallafi : Gazal Abdu Tassawa
Edita : Abdourahamane Hassane

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani