1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ban Ki-moon zai halarci taron koli na AU

Lateefa Mustapha Ja'afarJanuary 29, 2015

Babban magatakaradan Majalisar Dinkin Duniya zai yi tattaki zuwa cibiyar AU a Addis Ababa, inda zai tattauna da shugabannin Afirka kan matsalar Boko Haram

https://p.dw.com/p/1ESvv
Ban Ki-moon
Hoto: AFP/Getty Images/F. Coffrini

Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon zai halarci taron shugabannin kasashen kungiyar Gamayyar Afirka ta AU da za a gudanar a birnin Addis Ababa na kasar Ethiopiya. Kakakinsa Stephane Dujarric ne ya shaida wa manema labarai haka a birnin New York na kasar Amirka.

Taron zai mayar da hankali ne kan kungiyar Boko Haram da a yanzu ta addabi tarayyar Najeriya. Ban Ki Moon, ya ce zai yi kokarin karfafa wa shugabannin Afirkan gwiwa wajen nemo mafita kan barazanar da Boko Haram ke haddasawa a kasashen nahiyar a yanzu.