1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi Siriya da Ƙungiyar IS da aikata laifukan yaƙi

August 27, 2014

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana hakan a cikin rahoton da hukumar kula da hakkin ɗan Adam ta majalisar ta wallafa a wannan Laraba a birnin Geneva.

https://p.dw.com/p/1D2mu
Irak islamischer Staat Kämpfer Januar 2014
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya game da hakin ɗan Adam ya ce dakarun gwamnatin Siriya da mayaƙan adawa na 'yan Jihadi sun aikata manyan laifuka a kan ɗan Adam a cikin yakin basasar ƙasar. Rahoton ya ce dakarun Shugaba Bashar al-Assad sun yi amfani da guba a wasu lamura daban-daban guda takwas a yammacin ƙasar a watannin Afrilu da Mayu. Sai dai bai yi karin bayani ba. Sannan dakarun na Assad na ci gaba da aikata ta'asa ciki har da laifukan yaƙi. Rahoton da ya tattara hirarraki 480 da wasu tarin bayanai ya kuma taɓo batun keta hakkin dan Adam da ƙungiyoyin 'yan Islama suka aikata a Siriya. Kana suna tilasta wa kananan yara daukar makami. Akalla mutane dubu 190 aka kashe a rikicin na Siriya da aka fara a shekarar 2011.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Abdourahamane Hassane