An tabbatar da mutuwar daliban Mexiko
January 28, 2015Talla
Babban mai shigar da kara na kasar Mexiko Jesus Murillo ya ce babu tantama daukacin daliban kasar 43 da suka bace tun watan Satumban da ya gabata sun mutu. Ya ce an yi kuskuren zaton cewa daliban suna cikin wani bangaren gungun masu aikata laifuka.
An soki yadda gwamnatin kasar ta tunkari lamarin bacewar daliban, yayin da iyalai ke cewa wannan bayani bai gamsar ba. Dubban 'yan kasar ta Mexiko sun yi gangami tir da bacewar daliban, inda suke neman ganin an nemo daliban a mace ko a raye. Lamarin ya bata sunan gwamnatin Shugaba Enrique Pena Nieto.