1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace ma'aikatan MDD a Sudan

Usman ShehuJanuary 29, 2015

Wasu mutane dauke da makamai sun tilasta wa jirgin rarraba abinci na MDD a Sudan saukar dole, kana da yin awun gaba da jami'an da ke cikin jirgin

https://p.dw.com/p/1ESTq
Sudan Sudan People's Liberation Movement-North
Hoto: DW

An kama ma'aikatan na Majalisar Dinkin Duniya 'yan kasar Bulgeriya shida, a kasar ta Sudan yayin da suke kan aiki. Mutanen da ake aikin samar da abinci, an tilastawa jirginsu mai saukar angulu sauka, a yankin da gwamnati da 'yan tawaye ke fada da juna. An dai yi imanin cewa 'yan tawayen SPLM su ne suke rike da ma'aikatan na Majalisar Dinkin Duniya.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu