1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kwashe mata da kananan yara daga Yola

Muntaqa Ahiwa daga Yola/SBMay 21, 2015

Hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya NEMA, ta tabbatar da kwashe wasu mata da kananan yara akalla 275 daga sansanin gudun hijira da su ke ciki a Yola.

https://p.dw.com/p/1FTxa
Nigeria,Yola Malkohi Flüchtlingscamp Bild 8
Hoto: DW/Jan-Philipp Scholz

Jami'in hukumar na jihar Adamawa Malam Saad Bello, ya ce ofishin mai bada shawara kan harkokin tsaron kasa ne ya kwashe mata da yaran a jiya Laraba, sai dai shi ma jami'in bai san takamaiman wajen da aka kai su ba a halin yanzu.

Rashin sanin wajen da mutanen su ke dai na ci gaba da zama abin muhawara a jihar ta Adamawa, wadda ko a bayan-bayan nan ma ta fuskanci harin kunar bakin wake a kasuwar garin Garkida dake arewacin jihar, harin da aka dora alhakinsa a kan 'yan Boko Haram.