1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kama 'yan kungiyar 'yan uwa Musulmi 516

Ahmed SalisuJanuary 26, 2015

Rundunar 'yan sanda Masar ta kame 'yan kungiyar 'Yan Uwa Musulmi 512 biyo bayan tashin hankalin ya barke yayin bikin tunawa da ranar da guguwar neman sauyi.

https://p.dw.com/p/1EQno
Ägypten Präsident Al-Sisi
Hoto: imago/Xinhua

Ministan ma'aikatar cikin gidan Masar din Mohamed Ibrahim ya shaidawa manema labarai a birnin alkahira cewar an kama mutanen ne da laifin yin harbe-harbe da kuma dasa ababan fashewa baya ga lalata wasu wurare da suka yi sanadiyyar fashewar bam din da suka sanya.

To sai dai a daura da wannan, kungiyoyi na kare hakkin bani Adama daga ciki da wajen kasar na cigaba da sukar lamirin gwamnati na amfani da karfin da ya wuce kima wajen tarwatsa masu zanga-zanga, inda suka bukaci da a gudanar da bincike kan rikicin na jiya da ya yi sanadin rasuwar mutane sama da 20.