1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari kan mayaka a yammacin Tripoli na Libiya

Salissou BoukariSeptember 15, 2014

Wani jirgin yaki da ba a tantace ba, ya kai hari kan wani barakin soja da ke hannun mayaka masu adawa da gwamnati a yankin Gharyan da ke yammacin kasar.

https://p.dw.com/p/1DCgf
Libyen/ Kämpfe /Tripolis
Hoto: Reuters

A cewar kamfanin dillancin labaran kasar ta Libiya, Lana, harin dai ya taba wani wurin ajiye makammai da ke hannun mayakan a birnin Gharyan da ke a nisan kilomita 120 a kudu maso yammacin birnin Tripoli. Harin ya kuma haddasa jikkatar mutane da dama, yayin daga nashi bangare gidan Telebijin din Al-Nabaa ya sanar cewa mutane akalla 11 sun ji rauni.

Su dai wadannan mayaka na Gharyan, na daga cikin gungun mayakan Fajr Libiya, wata kungiya da ta kumshi kabilu daban-daban na kasar, wadanda suka yi nasarar karbe iko a birnin Tripoli a watan August da ya gabata, bayan da suka fatattaki mayakan Zenten da ke rike da filin jirgin saman birnini.