1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka Za ta riɓanya yawan sojojinta a Laberiya

Abdourahamane HassaneSeptember 30, 2014

Amirka ta ce za ta riɓanya addadin sojojinta da ke a Laberiya domin taimaka wa wajen daƙile cutar Ebola da ke yin barazana a yankin yammancin Afirka baki ɗaya.

https://p.dw.com/p/1DNRN
UN Vollversammlung 24.09.2014 - Barack Obama
Hoto: Getty Images/A. Burton

Tun da farko Amirkan ta aike da sojojinta kusan dubu uku waɗanda za su kula da aikin gina cibiyoyin yaƙi da cutar tare da ba da horo ga sauran jami'an kiwon lafiya da kuma na sa kai

da ya ke yin jawabi a zauren taron Mjalisar Ɗinkin Duniya, ministan harkokin waje na Laberiya ya ce cutar ta Ebola babban bala'i ne. A ƙasar ta Laberiya dai ya zuwa yanzu cutar ta kashe mutane 1830 yayin da a Guinea da Saliyio addadin waɗanda suka cikka da cutar ya kai dubu uku.